Wasanni

Sharhi kan yadda wasannin kwata finals na gasar zakarun Turai za su gudana

Informações:

Synopsis

Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya maida hankali ne kan yadda wasannin matakin kwata finals na gasar zakarun Turai za su gudana. A ranar Juma’ar da ta gabata ce dai hukumar kula da wasan kwallon kafar Turai UEFA ta hada yadda kungiyoyi 8 da suka yi saura a gasar zakarun Turai z asu kara da junanansu. Tsohon kyaftin din Najeriya wanda kuma ya taba lashe gasar da kungiyar Chelsea Mikel John Obi ne ya jagoranci hada yadda kungiyoyin za su kara da juna. Arsenal za ta fafata da Bayern Munich, Atletico Madrid za ta kece raini da Borussia Dortmund, Real Madrid ta kara da Manchester City ya yin da Paris Saint-Germain za ta kara da Barcelona.Ku letsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......